Notice: Function _load_textdomain_just_in_time was called incorrectly. Translation loading for the td-cloud-library domain was triggered too early. This is usually an indicator for some code in the plugin or theme running too early. Translations should be loaded at the init action or later. Please see Debugging in WordPress for more information. (This message was added in version 6.7.0.) in /home/taskirac/public_html/wp-includes/functions.php on line 6121
Lokaci yayi da matasa zasu maida hankali wajen koyon Sana’o’in hannu – Dr Sabo Wada Dutse | Taskira Online Magazine
Tuesday, November 18, 2025
HomeHausaLokaci yayi da matasa zasu maida hankali wajen koyon Sana'o'in hannu -...

Lokaci yayi da matasa zasu maida hankali wajen koyon Sana’o’in hannu – Dr Sabo Wada Dutse

by Kabiru Getso

Shugaban Kwalejin kimiyya da Fasaha ta Tarayya dake Kazaure (Husaini Adamu Federal Poly Technique Kazaure) Dr Sabo Wada Dutse ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da manema labarai.

Yace babu shakka wajibi ne matasa dama iyayen matasan su bada himma wajen koyan Sana’ar dogaro da kai komai kankantarta musammanan a wannan halin da ake ciki na karancin guraben ayyuka a Gwamnatoci.

Dr Sabo ya Kara da cewar hakan ne yasa Kwalejin ta himmatu wajen samar da kwasa kwasai da kuma kayayyakin koyar da Sana’oin hannu domin inganta rayuwar Daliban kwalejin dama sauran al’umma.

Kazalika Dr Sabo yayi kira da masu rike da madafun iko dama sauran al’umma musamman masu hannu da shuni da su cigaba da hobbasa wajen tallafawa harkar ilimin matasa domin shine hanyar da za’a samu saukin rashin tsaro da kuma rashin aikin yi da ya addabi matasa.

Bugu da kari ya ja hankalin dalibai da suyi aiki tukuru wajen neman ilimi tare da koyan Sana’a yadda ya kamata don taimakawa kansu dama sauran al’umma baki daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

FOLLOW US:

6,985FansLike
1,458FollowersFollow
553SubscribersSubscribe

Most Popular