Ibrahim Bello Gusau Ibg
Mai girma gwamnan jahar zamfara, Hon. Bello Muhammad (Matawallen Maradun), ya aminta da nada Yusuf Idris a matsayin direktan yada labarai na ofishin sa.
Kafin nadin shi, Yusuf Idris, direktan yada labarai ne a ofishin tsohon mataimakin gwamnan jaha Malam Ibrahim Wakkala Muhammad kuma kwararren danjarida ne da ya dade a cikin wannan aiki na jarida.
A madadin daukacin magoya bayan G8, muna mi ka kyakykyawar godiyar mu ta musamman ga mai girma sabon gwamnan jahar zamfara, Hon. Bello Muhammad (Matawallen Maradun) akan wannan karamci.
Haka zakika muna taya sabon direktan yada labarai na mai girma sabon gwamna samun wannan mukami, da fatar Allah ya sa a wanye lafiya.